Za a komawa zaman tattaunawa a Sudan
A yau lahadi ake sa ran sake komawa zaman tattaunawa tsakanin masu zanga-zanga da majalisar sojin dake rike da mulkin kasar Sudan a Khartoum dake babban birnin kasar.
Wallafawa ranar:
Daga cikin kungiyoyin da aka aikewa da goron gayata za iya zana wakilan kungiyoyin adinai da suka taka gaggarumar rawa a baya. Majalisar sojin kasar ce ta sanar da sake komawa tattaunwa da kungiyoyi da ma jam’iyyu a yau don samar da mafita da za ta kaisu ga samar da Gwamnatin rikon kwariya da za a dorawa nauyin shirya zaben kasar kamar dai yadda jama’a suka yi fata.
Kasar ta Sudan ta fada cikin rikici ne tun bayan saukar Shugaban kasar Omar El Beshir.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu