Isa ga babban shafi
Libya

Sojin Libya sun samu manyan makaman yakar Haftar

Rundunar sojin Libya da ke biyayya ga gwamnatin mai samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da karbar kayakin yaki ciki har da motoci da manyan makamai a wani mataki na ganin ta hanawa Khalifa Haftar kwace iko da Tripoli babban birnin kasar.

Wasu sojojin Libya masu biyayya ga gwamnati mai samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya
Wasu sojojin Libya masu biyayya ga gwamnati mai samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya Photo: Mahmud Turkia/AFP
Talla

Cikin sanarwar da ta fitar, rundunar sojin ta Libya ta ce yanzu ta na da tarin makaman da za ta kare al’ummar birnin na Tripoli daga mamayar Khalifa Haftar wanda ke rike da kaso mai yawa na yankunan kasar.

Ko da ya ke rundunar sojin ba ta sanar da inda ta samu makaman ba, amma rahotanni na nuni da cewa anga tarin motoci masu silke kirar kasar Turkiyya na sintiri a tsakiyar birnin na Tripoli.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.