Bakonmu a Yau
Mamman Danbuzuwa kan tabarbarewar matsalar tsaro a yankin Sahel
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:20
Matsalar tsaro na ci gaba da tabarbarewa a yankin Sahel, lura da yadda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da Faransawa a wani gandun dajin Jamhuriyar Benin, sai kuma hare-hare a kan mabiya darikar Katolika a Burkina Faso, da kuma wasu hare-hare biyu mabambanta jiya litinin a Jamhuriyar Nijar.Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen yammacin duniya da suka hada da Faransa, Amurka, Jamus har da Italiya suka jibge dubban sojoji a wannan yankin.Abdoulkarim Ibrahim Shikal, ya tuntubi Mamman Danbuzuwa, masanin lamurran tsaro a birnin Damagaram, domin jin yadda yake kallon wannan matsala.