Isa ga babban shafi
Afrika

Sabuwar zanga-zanga a Tripoli

A babban birni Tripoli na kasar Libya dubban jama’a ne sanye da riguna kalar dorowa suka gudanar da zanga-zanga nuna adawa da janar Haftar da yanzu haka dakarun sa suka kaddamar da yaki na karbe ikon Tripoli.Masu zanga-zangar sun kuma la’anci Faransa da suke zargi da goyawa Janar Haftar baya.

Janar Haftar a fadar sa dake birnin Bhengazi na kasar Libya
Janar Haftar a fadar sa dake birnin Bhengazi na kasar Libya REUTERS/Esam Omran Al-Fetori
Talla

A dai-dai lokacin da wannan zanga-zanga ta kuno kai a Libya ,Amurka ta fito fili tareda bayyana goyan bayan ta zuwa Janar Haftar,rahotanni sun nuna cewa Janar Haftar ya tattauna ta wayar talho da Shugaban Amurka Donald Trump.

Wasu kasashen Duniya na sukar matakin Amurka bayan da al’umar Tripoli suka bayyana adawa da matakan soja daga Janar Haftar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.