Isa ga babban shafi
Kamaru-Najeriya

Kamaru za ta maido da 'yan Najeriya dubu 4 gida

Hukumomin Kamaru sun bayyana cewar sun shirya tsaf domin mayar da 'yan Najeriya 4,000 da ke gudun hijira a kasar sakamakon rikicin kungiyar Boko Haram.

Wasu daga cikin 'yan gudun hijirar Boko Haram
Wasu daga cikin 'yan gudun hijirar Boko Haram Reinnier KAZE / AFP
Talla

Gwamnan Lardin Arewa Mai nisa, Midjinyawa Bakari ya bayyana cewar daga ranar 29 ga watan nan za su fara mayar da 'yan gudun hijirar da ke sansanin Minawao, wadanda suka bayyana aniyarsu ta komawa gida don ratsin kansu.

Bakari ya ce, sun tattauna da hukumomin Najeriya kuma sun amince da shirin mayar da 'yan gudun hijirar da suka fito daga Jihar Adamawa.

Rahotanni sun ce, shirin mayar da 'yan gudun hijirar bai shafi wadanda suka fito daga Jihar Barno ba, saboda rashin kwanciyar hankali a yankunansu.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce, sansanin Minawao ya karbi baki 'yan gudun hijira 57,000 daga Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.