Golden Eaglets ta isa Tanzania don fafatawa a gasar cin kofin Afrika
Tawagar kungiyar kwallon kafar Najeriya ta ‘yan kasa da shekaru 17 Golden Eaglets ta bar Abuja zuwa Tanzania don taka leda a gasar cin kofin Nahiyar Afrika ta ‘yan kasa da shekaru 17 karo na 13 da za ta fara gudana ranar 14 zuwa 28 ga watan nan.
Wallafawa ranar:
Golden Eaglets wadda ta dage kofin duniya har sau biyar, ta samu tikitin zuwa Tanzaniyar ne bayan nasara a gasar WAFU ta kasashen yammacin Afrika cikin watan Satumban bara a Jamhuriyar Nijar, bayan da ta lallasa Ghana da kwallaye 3 da 1 a wasan karshe.
Yanzu haka dai tawagar ta Golden Eaglets wadda ta halarci makamanciyar gasar har sau 9 ta kuma lashe sau 2 a shekarar 2001 da 2007 na cikin kasashen Afrika 4 da za a ga tutarsu a gasar cin kofin duniya ta ‘yan kasa da shekaru 17 da Brazil za ta karbi bakonci.
Yayin gasar ta tsawon mako guda a Tanzania dai, Golden Eaglets wadda ke rukunin A za ta kara da mai masaukin baki Tanzania kana Uganda sai kuma Angola.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu