Isa ga babban shafi
Mali

Adadin Fulanin da mahara suka hallaka a Mali ya karu

Adadin mutanen da suka mutu sakamakon harin da wasu mafarauta suka kaiwa Fulani a Mali ya karu daga 134 zuwa 157, abinda ke nuna cewa harin, shi ne irinsa mafi muni a tarihin kasar.

Daya daga cikin gidajen Fulani da mahara suka kone a harin da suka kai kan kauyen Ogassogou-puel da ke yankin tsakiyar kasar Mali.
Daya daga cikin gidajen Fulani da mahara suka kone a harin da suka kai kan kauyen Ogassogou-puel da ke yankin tsakiyar kasar Mali. Malian Presidency/Handout/Reuters
Talla

Kakakin gwamnatin kasar ta Mali Amadou Kotia ne ya bayyana karuwar adadin, tare da bayyana fargabar cewa akwai yiwuwar sake samun Karuwar yawan wadanda suka hallaka.

Harin na zuwa ne kasa da mako guda bayan wasu Yan bindiga sun kai hari kan barikin sojin Mali inda suka kashe 23 daga cikin su.

A ranar Lahadi da ta gabata, Gwamnatin Mali ta kori wasu manyan jami’an sojinta, sakamakon farmakin da aka kai kan kauyen Ogassogou da ke yankin tsakiyar kasar inda aka yiwa Fulanin kisan kiyashi

Zalika a farkon makon Gwamnatin ta Mali ta kuma rushe kungiyar Ambassagou ta mafarautan kabilar Dogon, wadanda ake zargi da kai kazamin harin.

Wadanda suka tsira sun zargi mafarautan kabilar Dogon da kai mumunan harin, kabilar da aka zarga da hallaka Fulani 37 a kauyen Koulogon da ke yankin tsakiyar kasar ta Mali cikin watan Janairu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.