Isa ga babban shafi

Kotu ta dakatar da dan takarar gwamnan Kano na Jam'iyyar PDP

Babbar kotun jihar Kano ta dakatar da takarar Abba Kabir Yusuf da ke neman kujerar gwamnan jihar karkashin jam’iyyar PDP, bisa hujjar rashin gudanar da zaben fidda gwani.

Dan takarar kujerar Gwamna a karkashin Jam'iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf.
Dan takarar kujerar Gwamna a karkashin Jam'iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf. Daily Post Nigeria
Talla

Zaman sauraron shari’ar karkashin Alkali Ambrose Lewis a yau Litinin ya ce Jam’iyyar ta PDP ba ta fitar da Abba Kabir Yusuf a tsarin da ya dace wajen fitar da dan takara ba.

Lauyan masu shigar da kara Kabiru Usman, ya ce dole ne Jam’iyyar ta PDP ta sake tsayar da dan takara na daban gabanin zaben gwamnoni a ranar 9 ga watan nan.

Sai dai lauyan PDP, Bashir Yusuf ya ce hukuncin kai tsaye bai shafi Abba Kabir Yusuf ba, face jam’iyyar ta PDP wadda ke da zaben sake gudanar da zaben fidda gwani.

A cewar Bashir Yusuf, Jam'iyyar ta PDP za ta bi umarnin Kotu don tabbatar da nasararta a zabe mai zuwa.

Hukuncin na Kotu dai na da nasaba da karar da Ali Amin Little ya shigar gaban kotun wanda ya ke kalubalantar matakin da Jam'iyyar ta bi wajen fitar da dan takarar gwamnan a jihar Kano.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.