Taron kawo karshen rikicin Libya da kuma shirya zaben kasar
Shugaban gwamnatin Libiya da kasashen Duniya ke goyon baya Fayez al-Sarraj da abokin hamayyarsa da tsagin sojin kasar ke yiwa Biyayya Khalifa Haftar, sun cimma yarjejeniyar shirya zabuka a kasar, da nufin kawo karshen yake-yaken da aka shafe tsawon lokaci ana gwabzawa, bayan hambarar Mu’ammar Ghaddafi.
Wallafawa ranar:
Shugabannin biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar ce a Abu Dhabi, domin dukunle gwamnatoci biyun da suke jagoranta a kasar ta Libya.
Tun a watan Mayu na shekara ta 2018, bangarorin biyu suka cimma yarjejeniyar shirya zabukan na Libya a karshen shekarar, amma sabon fadan da ya barke tsakaninsu ya jinkirta sa hannu da kuma aiwatar da yarjeniniyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu