PDP ta yi watsi da sakamakon zaben shugaban kasa
Babbar Jam'iyyar adawa a Najeriya PDP ta yi watsi da sakamakon zaben shugaban kasa da hukumar zaben kasar INEC ke ci gaba da aikin sanarwa a yau Litinin.
Wallafawa ranar:
A wani taron manema labarai da PDP ta kira, shugaban jam'iyyar na kasa Uche Secondus ya ce hukumar ta INEC na fifita jam'iyya mai mulki ne a sakamakon.
Cikin kalamansa Mr Secondus ya ce sakamakon da INEC ke sanarwa babu gaskiya a cikinsa, face sinkin murda-murda da magudi.
Yanzu haka dai hukumar zaben Najeriyar ta sanar da sakamakon jihohi 5 ne na Najeriyar inda Jam'iyya mai mulki ke da rinjayen kuri'u.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu