Bayan sanar da dage zaben Shugaban Najeriya zuwa ranar 23 ga watan Fabrairu daga hukumar zaben kasar ta INEC,yan kasar na ci gaba da bayyana tsokacin su a kai,yayinda yan siyasa ke zargin junan su da shirya magudi, a yau Laraba jam’iyya ta APC mai mulkin Najeriya tayi watsi da zargin dan takarar Jam’iyyar PDP Atiku Abubakar da cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari na yiwa dimokiradiya zagon kasa wajen mulkin kama karya.Bashir Ibrahim Idris a cikin shirin Dandalin siyasa ya mayar da hankali zuwa ga batun zaben na Najeriya.