Isa ga babban shafi
Afrika

Kasashen Saharar Afrika 28 sun haramta auren jinsi - bincike

Wani Bincike ya nuna cewar sama da rabi na kasashen Afirka da ke Yamma da Sahara na amfani da dokar haramta auran jinsi, yayin da sauran suka samar da yanayin dokokin da ke kare irin wadanan mutane.

Wasu maza ma'aurata kenan da ke cike da farin ciki bayan da kotun India ta halasta auren jinsi
Wasu maza ma'aurata kenan da ke cike da farin ciki bayan da kotun India ta halasta auren jinsi REUTERS/Francis Mascarenhas
Talla

Kungiyar kare hakkin Bil Adama ta Human Rights Watch ta ce kasashe 28 daga cikin 49 na da dokokin da ke hukunta masu irin wannan dabi’ar da ta shafi auran jinsi.

Neela Ghoshal, jami’ar kungiyar ta ce kasashe irin su Mauritania da Sudan da Arewacin Najeriya na amfani da hukuncin kisa kan irin wadanan mutane, duk da ya ke babu wani da aka bayyana cewar an aiwatar masa da hukuncin.

Sai dai kasashe irin su Angola da Mozambique da Seychelles sun yi watsi da irin wadannan dokoki, yayin da Chadi da Uganda suka gabatar da sabbin dokoki masu tsauri akan irin wadannan mutane.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.