Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo

Jam'iyyar shugaba Kabila ta lashe zaben 'yan majalisu

Gamayyar jam’iyyun da ke kawance da shugaban Jamhuriyar Congo Joseph Kabila, sun lashe zaben ‘yan majalisun kasar da gagarumin rinjaye.

Jami'an hukumar zaben CENI a Congo
Jami'an hukumar zaben CENI a Congo 路透社。
Talla

Sakamakon da hukumar zaben kasar CENI ta fitar a yau Asabar ya nuna cewa jam’iyyun kawancen na gwamnati sun lashe kujeru 280, daga cikin 429 da aka bayyana, yayinda ‘yan adawa suka samu kujeru 141.

Halin yanzu sakamakon zaben kujeru 71 ake ci gaba da dakon bayyanawa, a zaben majalisar Jamhuriyar Congon mai jimillar kujeru 500.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.