Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

Fayulu ya bukaci kotun koli ta soke zaben Jamhuriyar Congo

Martin Fayulu dan takarar ‘yan adawa da yazo na biyu a zaben shugabancin Jamhuriyar Congo, ya shigar da kara kotun kolin kasar, inda ya bukaci ta soke sakamakon zaben, saboda magudin da yake zargin an tafka.

Martin Fayulu dan takarar ‘yan adawa da yazo na biyu a zaben shugabancin Jamhuriyar Congo.
Martin Fayulu dan takarar ‘yan adawa da yazo na biyu a zaben shugabancin Jamhuriyar Congo. Reuters
Talla

Fayulu wanda ke ikirarin shi ne ya lashe zaben da ya gudana a ranar 30 ga watan Disamba, ya zargi Wanda hukumar zaben kasar ta baiwa nasara Felix Tshisekedi da cimma yarjejeniyar sirri da shugaba mai ci Joseph Kabila wajen murde zaben.

Nasarar Tshisekedi a zaben kasar ta Jamhuriyar Congo dai ta gamu da turjiyar, sauran ‘yan adawa, tawagar masu sa’ido ta kasashen turai, da kuma majalisar shugabannin cocin katolika na kasar mai wakilai dubu 40,000, wadanda suka ce sakamakon zaben ba sahihi bane.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.