Cocin Katolika a Congo ta ce ta san wanda ya lashe zaben kasar
Wallafawa ranar:
Kunna - 20:18
Martin Fayulu da ya zo na biyu a zaben shugabancin kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo, ya ce, zai daukaka kara a kotun fasalta kundin tsarin mulki don kalubalantar sakamakon zaben da ya ayyana Felix Tshisekedi a matsayin wanda ya lashe.Jam’iyyar Fayulu na ikirarin cewa, dan takarsu ya samu kashi 61 na kuri’un da aka kada sabanin kashi 34.8 da hukumar zaben kasar ta ce, ya samu, in da kuma Tshisekedi ya samu kashi 38.57.Tuni dai kasashen duniya ke ta mayar da martani game da wanan zabe.Garba Aliyu Zaria ya mayar da hankali zuwa wannan labari dama wasu labaren can daban a cikin shirin mu zagaya Duniya.