Isa ga babban shafi
Najeriya

Kar ku sake zabar gwamnan da ya gaza biyan hakkin ma'aikata- Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci ‘yan Najeriya su guji sake zaben duk wani gwamna da ya gaza biyan hakkokin ma’aikata a tsawon lokacin da ya dauka ya na shugabanci duk da kudaden da jihohin ke samu daga gwamnatin kasar.

Muhammadu Buhari wanda ke ci gaba da yakin neman zabensa a sassan kasar, ya ce abin takaici yadda gwamnonin kasar ke gaza sauke nauyin da ke kansu na hakkin ma'aikata amma kuma su ke kara tsayawa takara don a zabe su.
Muhammadu Buhari wanda ke ci gaba da yakin neman zabensa a sassan kasar, ya ce abin takaici yadda gwamnonin kasar ke gaza sauke nauyin da ke kansu na hakkin ma'aikata amma kuma su ke kara tsayawa takara don a zabe su. Reuters
Talla

Muhammadu Buhari wanda ke neman kujerar shugabancin Najeriyar a zagaye na biyu karkashin Jam’iyyar APC ya ce yana takaicin yadda gwamnoni ke iya barci cikin nutsuwa alhalin sun gaza biyan albashin ma’aikata.

A zantawarsa da wata kafar yada labaran Amurka, Muhammadu Buhari ya ce rashin adalci ne gwamnonin su juyar da hakkokin ma’aikata don wasu abubuwa na kashin kansu bayan karbar kudade daga hannun gwamnatin kasar.

Ba tun yanzu ba dai shugaban Najeriyar ke kokawa da yadda gwamnatocin jihohin kasar ke gaza sauke nauyin ma'aikata ciki har da wadanda suka yi ritaya tsawon lokaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.