Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Farfesa Khalifa Dikwa kan yadda Buhari ya amince cewa an fuskanci koma baya a yaki da Boko Haram

Wallafawa ranar:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince cewa ana samun koma-baya a fafutukar kakkabe mayakan Boko Haram musamman a yankin arewa maso gabashin kasar.A yayin wata hirarsa da aka watsa ta kafar talabijin ta Arise a cikin daren da ya gabata, shugaba Buhari ya amince cewa, sojojin kasar na fuskantar matsin lamba daga mayakan na Boko Haram da ke amfani da salon yakin sunkuru. Shugaban ya kuma amince cewa, sojojin kasar na fama da matsalar rashin karfafa musu guiwa a fagen-daga, amma ya ce, suna kan kokarin shawo kan wannan matsalar. Hakan muka tuntubi Farfesa Khalifa Dikwa ga kuma abin da ya ke cewa.

Hare-haren Boko Haram a baya-bayan nan musamman kan dakarun sojin Najeriyar na ci gaba da tsananta inda a lokuta da dama suke hallaka tarin jami'an sojin da na 'yan sanda.
Hare-haren Boko Haram a baya-bayan nan musamman kan dakarun sojin Najeriyar na ci gaba da tsananta inda a lokuta da dama suke hallaka tarin jami'an sojin da na 'yan sanda. Edwin Kindzeka Moki/AP/SIPA
Sauran kashi-kashi
  • 03:16
  • 03:19
  • 03:26
  • 03:17
  • 03:40
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.