Isa ga babban shafi
Sudan

Sudan: 'Yan adawa sun bukaci El-bashir ya sauka daga mulki

‘Yan adawa a Sudan sun bukaci shugaban kasar Umar Al-bashir da ya gaggauta sauka daga karagar mulki, bayan share sama da makonni biyu ana tarzomar nuna kin jinin mulkinsa.

Shugaban Sudan Omar Al Bashir, birnin Khartum ranar 31 disamba 2018
Shugaban Sudan Omar Al Bashir, birnin Khartum ranar 31 disamba 2018 ASHRAF SHAZLY | AFP
Talla

Ko a jiya juma’a sai dai ‘yan sanda suka yi amfani da hayaki mai sa kwalla domin tarwatsa jama’a da suka bukaci gudanar da zanga-zanga bayan kammala sallar juma’a.

A ranar 19 ga watan disambar da ya gabata ne aka fara zanga-zanga a kasar, bayan da gwamntin ta yanke shawarar kara kudin biredi, to sai dai mafi yawan masu tarzomar na neman samun karin ‘yanci ne a kasar da shugaba El-bashir ke mulki sama da shekaru 30.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.