Isa ga babban shafi
Algeria

Damuwa dangane da makomar wasu baki a Algeria

Hukumar kula da ‘yan gundun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce akwai damuwa matuka dangane da makomar wasu baki mafi yawansu ‘yan asalin kasashen larabawa da mahukuntan Algeria suka tsare a wani yankin da ke kudancin kasar.

Wasu daga cikin yan cin rani a Algeria
Wasu daga cikin yan cin rani a Algeria NBC News/IOM
Talla

Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin mutanen zai kai 120, da suka hada da yan Syria, Falesdinawa da kuma yan kasar Yemen, yanzu haka ana tsare da su ne a wani sansani da ke garin Tamarasset da ke iyakar kasar da jamhuriyar Nijar.

Da jiamawa ana zargin hukumomin Algeria da kaucewa batun kare hakokin bil Adam musaman  baki yan cin rani dake tsallakawa daga kasar zuwa Turai.

Ya zuwa yanzu hukumomin Algeria basu ce upon  dangane da wannan zargi daga hukumar kula da yan gudun hiijira.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.