Aminu Bala Sokoto kan fargabar da 'yan Najeriya ke ciki sanadiyyar karancin tsaro a Maiduguri da Zamfara
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:20
‘Yan a Najeriya a ciki da wajen kasar na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu dangane da matsalolin tsaron da ke ci musu tuwo a kwarya, musamman a jihar Zamfara da kuma Maiduguri, inda ake fama da hare-haren mayakan Boko Haram da na ‘yan bindiga.A baya bayan nan ne dai Tsohon shugaban hukumar tsaron farin kaya ta DSS na Najeriya Mista Mike Ejiofor, ya shawarci gwamnati da ta yi gagarumin garambawul na sauya baki dayan shugabancin hukumomin tsaron kasar, domin farfado da karsashin ayyukansu na kare rayuka da da dukiya. Micheal Kuduson ya tattauna da Aminu Bala Sokoto Squadaron leader mai ritaya, masananin tsaro a tarayyar Najeriya, wanda ya yi tsokaci akan wannan kalubale.