Isa ga babban shafi
Najeriya-Boko Haram

Burutai ya bukaci jajircewar sojin Najeriya a yaki da Boko Haram

Babban Hafson sojin kasa na Najeriya Manjo Janar Yusuf Tukur Burutai ya bukaci dakarun sojin kasar su tashi tsaye a yakin da su ke da Boko haram a yankin arewa maso gabashin kasar.

Babban Hafson sojin kasan na Najeriya Janar Yusuf Tukur Burutai ya dora laifin yada labaran karyar kan masu farfagandar ganin ba a kawo karshen yakin da Boko Haram ba.
Babban Hafson sojin kasan na Najeriya Janar Yusuf Tukur Burutai ya dora laifin yada labaran karyar kan masu farfagandar ganin ba a kawo karshen yakin da Boko Haram ba. AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Cikin sakonsa na Kirsimeti Burutai ya musanta zarge-zargen da ake na cewa har yaznu mayakan na Boko Haram su na da sauran karfi, inda ya ce a bayyana ta ke sojin Najeriya sun yi rawar gani wajen murkushesu.

A cewar Burutai cikin kalaman na sa da ke matsayin jan kunne ga Sojin na Najeriya, ka da su yarda bayanan karya da ake yadawa na kara yawan adadinsu da aka kashe a fagen daga ko kuma karfin da Boko Haram ke da shi ya rage musu karsashi, yana mai cewa kadan ya rage a ga bayan kungiyar.

Burutai ya dora laifin bayar da bayanan karya kan halin da ake ciki a yakin da Boko Haram kan masu farfagandar ganin sun rage karsashin dakarun.

Cikin jawaban na sa Janar Burutai ya yi fatan Dakarun su gudanar da bukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara cikin lumana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.