Faransa ta kai dauki zuwa Burkina Faso
Shugaban Burkina Faso Christian Kabore ya kai ziyara a Faransa inda ya tattauna da shugaban kasar ta Faransa Emmanuel Macron dangane da matsalar tsaron da kasar mai iyaka da Mali ke fama da ita.
Wallafawa ranar:
Faransa tsawon shekaru na taka gaggarumar rawa wajen dafawa kasashen Sahel a bangaren tsaro, tareda samar da kungiyar nan ta G5 Sahel da Nijar ke jagoranta, sai dai hakan bai hana yan ta’adda cigaba da kai hare-hare zuwa kasashen da suka hada da Burkina Faso.
karshen ganawar Shugaban Burkina Faso da Emmanuel Macron na Faransa , Faransa ta ce za ta bai wa jami’an tsaron Burkina Faso motocin Pick-up 34 domin karfafa masu gwuiwar yaki da ayyukan ta’addanci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu