Isa ga babban shafi
Turai

Kamfanonin Eni da Shell na da masaniya wajen baiwa wasu Najeriya cin hanci

Wata mai shari’a a kasar Italiya ta bayyana cewar kamfanonin hakar man Eni da Shell na da masaniyar cewar an baiwa wasu yan siyasa da jami’an gwamnati Najeriya cin hanci wajen cinikin rijiyoyin mai a shekarar 2011 a kasar.

Alamomin kamfanonin hakar man Feutr dake aiki a Najeriya
Alamomin kamfanonin hakar man Feutr dake aiki a Najeriya Reuters
Talla

Kamfanonin biyu sun sayi rijiyar mai lamba OPL 245 akan kudi sama da dala biliyan 1 da miliyan 300, yayin da yan siyasa da da wasu jami’an gwamnati suka yi rub da ciki da Dala biliyan guda da miliyan 100.

Mai shari’ar Giusy Barbara tace kamfanonin biyu na sane da wannan aika aika, abinda yasa aka daure mutane biyu da suka shiga tsakani wajen cinikin, Emeka Obi da Gianluca Di Nardo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.