Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Sudan ta Kudu za ta baiwa jami'an lafiyarta rigakafin Ebola

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, tace hukumomin Sudan ta kudu za su yiwa jami’an kula da lafiyar su allurar rigakafin cutar Ebola saboda mu’amalar da suke yi kusa da iyakar kasar da Jamhuriyar Congo.

Wasu ma'aikatan lafiya yayin tsaftace akwatin gawar wani mutum da ya mutu a dalilin cutar Ebola dake garin Beni a Jamhuriyar Congo. 13/8/2018.
Wasu ma'aikatan lafiya yayin tsaftace akwatin gawar wani mutum da ya mutu a dalilin cutar Ebola dake garin Beni a Jamhuriyar Congo. 13/8/2018. Photo: John Wessels/AFP
Talla

Ma’aikatar lafiyar kasar tace rigakafin da za ta yi tare da hukumar lafiyar, zai mayar da hankali kan jami’an ta dake aiki a Juba, Yei, Yambio da kuma Nimule.

Kasar Sudan ta kudu na daga cikin kasashen dake iyaka da Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo inda cutar ta hallaka mutane 271 ya zuwa yanzu.

A ranar 19 ga watan Disamba za’a soma aikin yiwa ma’aikatan lafiyar na Sudan ta Kudun rigakafi, kuma tuni aka ware maganin rigakafin na Ebola 2,160.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.