Isa ga babban shafi
Najeriya-Boko Haram

Burutai ya sake sauya kwamandan Operation lafiya dole

Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da gagarumar garambawul ga kwamandodin rundunoninta da ke yaki da kungiyar boko haram a sassan kasar.

Sabbin sauye sauyen dai sun shafi kwamandodi da dama a matakai daban daban.
Sabbin sauye sauyen dai sun shafi kwamandodi da dama a matakai daban daban. AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Daraktan yada labaran rundunar, Janar Sani Usman Kuka sheka, ya bayyana cewar an nada Manjo Janar OT Akinjobi a matsayin kwamandan runduna ta 3 da ke yaki da kungiyar boko haram, yayin da aka nada Manjo Janar MG Ali a matsayin kwamandan runduna ta 9, sai kuma Birgediya Janar BR Sinjen ya zama kwamanda runduna ta musamman da ke kai dauki.

Janar kuka sheka ya ce sauye sauyen sun shafi kwamandodi da dama a matakai daban daban.

A farkon makon nan ne Ministan tsaro Janar Mansur Dan Ali ya umurci shugaban rundunar sojin, Janar Tukur Buratai da ya koma Maiduguri da kuma aiwatar da sauye sauyen jami’an sojin domin sake fasalin yakin da suke da kungiyar boko haram.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.