Bakonmu a Yau
shuwagabanin kasashe 4 na yankin tafkin Tchadi na taro a injamena kan matsalar B/H
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:34
KAMAR Yadda watakila kukaji a cikin labaran duniya, yau shugabannin Kasashen Najeriya da Nijar da kuma Chadi zasu gudanar da wani taro a birnin Njamena domin tattauna karuwar hare haren kungiyar Boko Haram wadanda suka kai ga rasa dimbin rayuka.Wannan taro na zuwa ne kwana guda bayan wani taro da manyan hafsoshin sojin kasar Najeriya suka gudanar a birnin Maiduguri.Dangane da taron, mun tattauna da Dr Bashir Nuhu Mabai na Jami’ar Katsina, kuma ga tsokacin da yayi akai.