Isa ga babban shafi
Sahel

Iyalan Sophie Petronin na kira zuwa Shugaba Macron

Tsawon shekaru biyu babu duri’ar yar kasar Faransa nan Sophie Petronin da wasu yan bindiga suka yi awon gaba da ita a Gao dake kasar Mali.A jiya asabar daya daga cikin ya‘an ta Sebastien Chadaud Petronin a wata zantawa da manema labarai na Afp,Rfi da Radio Faransa ya bukaci Shugaban Faransa ya kara basu karin haske da kuma sanar da matsayar sa dangane da abinda hukumomin Faransa ke yi a kai.

Sophie Pétronin yar kasar Faransa da ake garkuwa da ita a yankin Sahel
Sophie Pétronin yar kasar Faransa da ake garkuwa da ita a yankin Sahel © AFP
Talla

Sebastien Chadaud Petronin da ya samu isa kasar Mauritania ya karasa da cewa kasancewar sa Afrika , ita ce ta neman shiga tattaunawa da masu garkuwa da mahaifiyar sa.

Idan aka yi tuni ranar 24 ga watan Disemba na shekara ta 2016 a birnin Gao wasu yan bindinga suka yi awon gaba da wannan mata mai shekaru 73.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.