Harin Tumour ya jefa jama’a cikin fargaba
Hankulan jama’a sun tashi a yankin Diffa da ke gabashin Jamhuriyar Nijar, bayan da wasu ‘yan bindiga da ake zaton cewa magoya bayan Boko Haram ne suka kashe mutane 8 da ke aiki da wani kamfanin haka riyoji mai suna Foraco a garin Toumour.
Wallafawa ranar:
Bayanai sun ce mutanen na gina rijiya ne domin jama’ar da ke rayuwa a sansanin ‘yan gudun hijira a garin Toumour, lamarin da a cewar kungiyoyin fararen hula a Diffa ba karamar matsala zai haifar wa makomar jama’a ba.
Harin da yan bindigan suka kai jiya da asuba a garin na Tumour ya wakana ne a dai dai lokacin da jami’an tsraro dake kula da kare lafiyar ma’aikantan kamfanin Foraco suka janye daga fadar magajin garin Tumour wurin da aka sauke ma’aikantan kamfanin Foraco.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu