Isa ga babban shafi
Somalia-Al-Shebab

Harin ta'addanci ya hallaka mutane da dama a Somalia

Akalla mutane 20 suka mutu yayinda da dama suka jikkata bayan tashin wasu bama-bamai da aka sanya cikin motoci a birnin Mogadisho na kasar Somaliya, yau juma’a.

Akwai dai kwakkwaran zaton cewa kungiyar Al-Shebab ce ta kaddamar da harin na yau ko da dai kawo yanzu ba ta fito ta dauki nauyinsa ba.
Akwai dai kwakkwaran zaton cewa kungiyar Al-Shebab ce ta kaddamar da harin na yau ko da dai kawo yanzu ba ta fito ta dauki nauyinsa ba. REUTERS/Feisal Omar
Talla

Majiyoyin labarai a kasar ta Somaliya sun tabbatar da cewa galibin mutanen da suka mutu a harin na yau fararen hula ne sai kuma tsirarun jami’an tsaro da ke kan hanya.

A cewar Ibrahim Mohammed babban jami’in dan sanda mai kula da birnin na Mogadisho, bama-baman biyu an sanya su ne a cikin Mota kuma bayan tashinsu ne na ukun ya kara ta shi a wani waje daban.

Wani ganau Hasan Adan, ya ce akasarin wadanda abin ya rutsa da su, mutane ne da ke tafe a cikin kananan motoci.

Kawo yanzu dai babu kungiyar da ta dauki alhakin harin sai dai akwai kwakkwaran zaton cewa kungiyar Al-Shebab ce ta kaddamar da shi, la'akari da yadda ta sha alwashin ganin bayan gwamnatin kasar ta Somaliya, mai samun gowon bayan kasashen duniya da ma sojojin kungiyar hadin kan Afrika dubu 20.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.