Isa ga babban shafi
Uganda-Ebola

Uganda za ta fara riga-kafin Ebola kan jami'anta na Lafiya

Hukumomin lafiya a Uganda sun sanar da aniyar fara gangamin rigakafin cutar Ebola a jibi Litinin don kaucewa barkewar cutar la’akari da yadda ake ci gaba da fuskantar annobarta a makociyar kasar Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo.

Matakin na Uganda na zuwa a dai dai lokacin da cutar ta Ebola ke kara kusanto kasar tazarar mil 60 tsakaninta da inda annobar ta fi ta'azzara a Jamhuriyar Congo.
Matakin na Uganda na zuwa a dai dai lokacin da cutar ta Ebola ke kara kusanto kasar tazarar mil 60 tsakaninta da inda annobar ta fi ta'azzara a Jamhuriyar Congo. REUTERS/Olivia Acland
Talla

A cewar ma’aikatar lafiyar Uganda yanzu haka za ta fara bayar da rigakafin ne daga kan jami’an lafiyarta musamman wadanda ke aiki gab da kan iyakar jamhuriyyar Demokradiyyar Congo tazarar mil 62 da yankin da ake fuskantar annobar.

Ministan lafiyar Uganda Jane Ruth Aceng ya ce yanzu haka sun aike da allurai dubu 2 da dari 1 ga jami’ansu da ke can kan iayakar kasar don bayar da kariya ga lafiyarsu kafin kai tsaye su dawo kan jami’ansu da ke aikin a cikin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.