Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Shugaban Sudan Ta Kudu Ya Saki Manyan 'Yan Tawaye Da Ke Tsare

Gwamnatin kasar Sudan ta Kudu ta saki wasu manya na hannun daman madugun ‘yan tawayen kasar Reik Machar da ake tsare dasu a gidan Kaso, domin cika wasu sharuddan dake kunshe cikin yarjejeniyar sulhu da bangarorin dake yaki a kasar suka sanya hannu.

Shugaba Salva Kiir  tare da madugun adawa  Riek Machar ranar  12 ga watan Satumba  2018.
Shugaba Salva Kiir tare da madugun adawa Riek Machar ranar 12 ga watan Satumba 2018. rfi
Talla

Mutane biyu daga ciki sun hada da wani tsohon sojan Africa ta Kudu da yayi ritaya William Endley wanda mashawarcin madugun adawan ne, sai kuma James Gatdet kakakin bangaren ‘yan tawayen wadanda  aka zartas masu da hukuncin kisa a chan baya.

Tun ranar laraba ne dai shugaban kasar Salva Kiir ya umarci a saki mutanen saboda cika sharuddan yarjejeniyar sulhu da aka kulla.

Mutane akalla dubu 383 aka kashe a yakin kasar da aka fara tun shekara ta 2013.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.