Shugaban Sudan Ta Kudu Ya Saki Manyan 'Yan Tawaye Da Ke Tsare
Gwamnatin kasar Sudan ta Kudu ta saki wasu manya na hannun daman madugun ‘yan tawayen kasar Reik Machar da ake tsare dasu a gidan Kaso, domin cika wasu sharuddan dake kunshe cikin yarjejeniyar sulhu da bangarorin dake yaki a kasar suka sanya hannu.
Wallafawa ranar:
Mutane biyu daga ciki sun hada da wani tsohon sojan Africa ta Kudu da yayi ritaya William Endley wanda mashawarcin madugun adawan ne, sai kuma James Gatdet kakakin bangaren ‘yan tawayen wadanda aka zartas masu da hukuncin kisa a chan baya.
Tun ranar laraba ne dai shugaban kasar Salva Kiir ya umarci a saki mutanen saboda cika sharuddan yarjejeniyar sulhu da aka kulla.
Mutane akalla dubu 383 aka kashe a yakin kasar da aka fara tun shekara ta 2013.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu