Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Dr Elharoon Muhammad kan komawar Riek Machar gida dama batun tattaunawar zaman lafiyar kasar

Wallafawa ranar:

Rahotanni daga birnin Juba na kasar Sudan ta kudu na cewa madugun ‘yan tawayen kasar, kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Reik Machar ya koma gida Juba bayan da ya kwashe sama da shekaru 2 ya na gudun hijira a ketare.Ya koma gida ne tun a jiya domin ya shiga zaman sulhu da sanya hannu cikin yarjejeniya da ake kallon ita ce ta karshe da za ta kai ga maido da zaman lafiya a kasar. Hakan ya sa muka tattauna da Dr Elharoon Muhammad masanin siyasar kasashen ketare ga kuma abin da ya ke cewa.

Shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa kuma jagoran 'yan tawayen kasar Riek Machar bayan isowarsa Juba jiya Laraba 31 ga watan Oktobon 2018.
Shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa kuma jagoran 'yan tawayen kasar Riek Machar bayan isowarsa Juba jiya Laraba 31 ga watan Oktobon 2018. REUTERS/Jok Solomun
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.