Isa ga babban shafi
Najeriya-Kaduna

Dokar takaita zirga-zirga ta dawo sabuwa a Kaduna

Gwamnatin Kaduna a yankin arewacin Najeriya ta sake maido da dokar takaita zirga ziraga tsawon sa'o'i 24 a ciki da kewayen jihar, wadda ta sassauta a Lahadin da ta gabata.

Dawo da dokar ta biyo bayan jita-jitar rikici a wasu sassa na jihar.
Dawo da dokar ta biyo bayan jita-jitar rikici a wasu sassa na jihar. Reuters
Talla

Matakin ya biyo bayan zaman dar-dar da jama’a suka sake fuskanta, bayan gano gawar Sarkin Kadara, mai rike da sarautar Agamo Adara, Maiwada Galadima, wanda aka sace a Juma’ar makon da ya gabata.

Dawo da Dokar dai na zuwa ne kwanaki hudu bayan sassauta dokar wadda aka sanya sakamakon wani tashin hankali da ya kai ga mutuwar mutane 55 a kasuwar magani da ke karamar hukumar Kajuru a jihar ta Kaduna.

Kaduna dai na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fuskantar matsalolin tsaro masu alaka da satar mutane don neman kudin fansa rikicin kabilu dama na addini.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.