Jamhuriyar Congo-Ebola
Ebola ta sake bulla a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo
Mahukunta a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo sun ce annobar Ebola ta bulla a wani yanki na daban da ke gabashin kasar, bayan da aka yi shelar cewa an shawo kan cutar bayan da ta kashe mutane 125 a cikin watannin da suka gabata.
Wallafawa ranar:
Talla
Ministan lafiyar kasar Oly Ilunga, ya ce annobar ta bulla ne a wani wuri da ke tsakiyar Beni, a lardin Kivu ta Arewa kusa da iyakar kasar da Uganda.
Ministan ya ce an samu bullar cutar a wannan yanki ne sakamakon yadda jama’a ke cigaba da bijire wa matakan mahukunta ke dauka domin hana yaduwar cutar ta Ebola
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu