Isa ga babban shafi
Kamaru

An samu tashin hankali a zaben Kamaru

Rahotanni daga kamaru sun ce, an samu yan tashe-tahsen hankula a sassan kasar da ake fama da matsalar 'yan aware yayin gudanar da zaben shugaban kasa, in da  aka soke kuri’u a wasu wuraren saboda fargabar matsalar tsaro.

An girke jami'an tsaro a yankin da shugaba Paul Biya ya kada kuri'arsa
An girke jami'an tsaro a yankin da shugaba Paul Biya ya kada kuri'arsa REUTERS/Zohra Bensemra
Talla

Rahotanni na cewa, jami’an tsaro sun harbe mutane uku da ake zargin cewa ‘yan aware ne daga Bamenda

Harbin na zuwa bayan zargin ‘yan awaren da kai farmaki kan jama’ar da ke kai–kawo a Bamenda, yayin da a ranar Juma’a ma  aka harbe wasu ‘yan awaren Ambazonia uku a birnin Buea.

Tuni aka rufe rumfunan zabe, in da a yanzu ake dakon sakamakon karshe da za a fitar a tsakanin kwanaki 15 kamar yadda dokar kasar ta tanada.

Ana kyautata zaton shugaba mai ci, Paul Biya mai shekaru 85 ya sake komawa kan kujerarsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.