Jami'an Tsaro A Kenya Na Tsare Da "Yan Kasar China 5 Dake Barazana Ga Tsaro
Jami'an tsaro a Kenya na tsare da wasu ‘yan kasar China biyar da aka same su da wasu tarkacen naurori na tsaro da suka fara dasawa a kasar da cewa suna son kafa kamfanin harkokin tsaro ne, duk da cewa basu da takardun izinin shiga kasar.
Wallafawa ranar:
Gwamnatin kasar na ta yada wannan kamu na ‘yan kasar China a wani lokaci da ake kukan yawaitan ‘yan China dake leburanci a Kenyan ganin akwai dimbin matasan Kenya marasa ayyukan yi.
Cikin kayayyaklin da aka samu a wajen su sun hada da kayan soja, wayoyin sadarwa na oba-oba, da kuma tulin gwangwanayen barkonun tsohuwa.
Yanzu haka ana tsare dasu kafin daukan mataki na gaba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu