Isa ga babban shafi
Angola

Dos Santos zai ajiye shugabancin jam'iyyar MPLA

A yau asabar toshon shugaban Angola Jose Eduardo dos Santos zai ajiye shugabancin jam’iyyar da ke kan karagar mulkin kasar MPLA, shekara daya bayan zaben da ya dora Joao Louranco a kan karagar mulki.

José Eduardo dos Santos tsohon shugaban Angola
José Eduardo dos Santos tsohon shugaban Angola © MARCO LONGARI / AFP
Talla

Mika ragamar jagorancin jam’iyar a hannun shugaba Louranco, na nufin kawo karshen shekaru 39 da tsohon shugaba dos Santos da kuma iyalansa suka share suna jan zarensu a kasar mai arzikin mai.

Hakazalika bikin mika jagorancin jam’iyyar da zai gudana a birnin Luanda, na zuwa ne a cikin wani yanayi na tsamin dangantaka tsakanin mutanen biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.