Boko Haram ta hallaka sojin Najeriya 30 a Borno
Rahotanni daga Najeriya na cewa akalla dakarun Sojin kasar 30 ne suka hallaka yayin wata fafatawarsu da mayakan Boko Haram a yankin arewa maso gabas da ke gab da kan iyakar kasar da Jamhuriyyar Nijar.
Wallafawa ranar:
Wasu majiyoyin Tsaro sun tabbatar da mutuwar dakarun kusan 30 tare da raunata da dama bayan wani farmaki da mayakan na Boko Haram suka kai sansaninsu.
A cewar Majiyoyin tun a ranar Alhamis ne wani adadi mai yawa na Mayakan Boko Haram din ya dirar sansanin Sojin Najeriyar da ke kauyen Zari a arewacin jihar Borno gab da kan iyaka, kuma bayan daukar tsawon lokaci ana fafatawa mayakan suka yi nasara fatattakar dakarun sojin tare da hallaka kusan 30.
A baya-bayan nan dai ana yawan samun kai farmaki kan dakarun sojin wanda a lokuta da dama akan hallakasu tare da tarwatsa wasu zuwa dazuka, inda ko a kwanakin baya an samu tarin dakarun sojin da suka bace a daji ko da dai shalkwatar rundunar sojin Najeriyar ta ce ba haka abin ya ke ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu