Isa ga babban shafi
Kenya

Kotu ta gurfanar da mataimakiyar shugaban kotun kolin Kenya

Yan Sanda a Kenya sun sanar da kama mataimakiyar shugaban kotun kolin kasar Philomena Mwilu saboda zargin da ake mata na karbar cin hanci da rashawa.

Mataimakiyar shugaban kotun kolin a Kenya Philomena Mwilu
Mataimakiyar shugaban kotun kolin a Kenya Philomena Mwilu citizentv.co.ke
Talla

Mai shari’ar na daga cikin alkalan kotun koli 7 da suka soke zaben shugaban kasar zagaye na farko da shugaba Uhuru Kenyatta ya lashe a watan Agustan bara, wanda ya haifar da rikici a kasar.

Darakatan gabatar da kara, Noordin Haji ya ce akwai sheidun dake nuna yadda mai shari’ar ta saba ka’idar aiki domin biyan bukatun kan ta da suka hada da karbar kudade da kyaututtuka da kuma kaucewa biyan haraji.

Kotu ta bada belin ta bayan gurfanar da ita a gaban shari’a akan kudi sule miliyan 5.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.