Isa ga babban shafi
Mali

Magoya bayan Cisse sun yi zanga-zanga a Bamako

Daruruwan magoya bayan dan takarar ‘yan adawa a zaben shugabancin Mali, Souma’ila Cisse, sun gudanar da zanga-zanga jiya Asabar a babban birnin kasar Bamako, domin nuna rashin amincewa da sakamakon da ya baiwa shugaba mai ci Ibrahim Boubacar Keita nasara da gagarumin rinjaye.

Magoya bayan Souma'ila Cisse dan takarar da ya sha kaye a zaben shugabancin Mali zagaye na biyu, a lokacin da suke zanga-zangar adawa da sakamakon zaben a birnin Bamako.
Magoya bayan Souma'ila Cisse dan takarar da ya sha kaye a zaben shugabancin Mali zagaye na biyu, a lokacin da suke zanga-zangar adawa da sakamakon zaben a birnin Bamako. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Magoya bayan na Cisse sun gudanar da zanga-zangar ce cikin sa idon ‘yan sandan kwantar da tarzoma, wadanda suka kasance cikin shirin ko ta kwana.

Tuni dai Cisse ya shigar da kara kotun kolin kasar domin kalubalantar zaben da ya ce an tafka magudi a cikinsa.

Sai dai tawagar da ta sa ido kan zaben na Mali daga kungiyar tarayyar turai da wasu takwarorinta na ciki da wajen kasar, sun ce duk da an fuskanci tangarda a wasu wuraren yayin gudanar da zaben, babu wata shaida da ke nuna an tafka magudin da ‘yan adawa ke zargi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.