Isa ga babban shafi
Mali

Guterres ya bukaci 'yan takarar zaben Mali su kai zuciya nesa

Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar kasashen Turai sun bukaci taka tsan tsan a Mali, bayan da dan takaran zaben shugaban kasa daga bangaren yan adawa, Soumaila Cisse ya ce ba zai amince da sakamakon zaben kasar ba.

Takardar zaben Shugabancin kasar Mali
Takardar zaben Shugabancin kasar Mali REUTERS/Luc Gnago
Talla

Sakatare Janar Antonio Guterres ya bukaci bangarorin biyu da su kwantar da hankalin har zuwa lokacin da za’a bada kammalallen sakamakon zaben, yayin da kungiyar kasashen Turai ta bukaci bangarorin da su kaucewa bayyana sakamakon na kashin kan su.

Tuni Cisse ya bukaci magoya bayan sa da su kwatowa kan su yanci kan sakamakon zaben.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.