Zaben Mali: Za a fafata a zagaye na biyu tsakanin Ibrahim Boubacar Keita da Soumaila Cisse
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:18
'Yan takara biyu da suka yi nasasar zuwa zagaye na gaba na zaben shugabancin kasar Mali sun fara tattaunawa da sauran ‘yan siyasar da suka sha kaye a zagayen farko na zaben, a yunkurunsu na kulla kawance.Sakamakon da hukumar zaben kasar ta fitar na nuni da cewa shugaba Ibrahim Boubacar Keita ne ke sahun gaba, da 41,4% yayin da abokin hamayyarsa na siyasar Soumaila Cisse ke da 17,8%.To domin jin yadda masana salon siyasar kasar ta Mali ke kallon wannan sakamako, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Tahirou Guimba, dan siyasa da ya tsaya takarar shugabancin Jamhuriyar Nijar a zaben da ya gabata, ga kuma abin da yake cewa.