Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo-Ebola

An kara samun barkewar Ebola a Jamhuriyar Congo

Gwamnatin Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo ta ce yanzu haka kasar na fuskantar barazanar barkewar wata sabuwar cutar Ebola, mako guda bayan kasar ta bayyana kawo karshen cutar wanda ta lakume rayukan mutane 33.

Rahotanni sun ce an fara daukar nau'in jinin masu fama da zazzafan zazzabin don tabbatar da basu dauke da cutar ta Ebola.
Rahotanni sun ce an fara daukar nau'in jinin masu fama da zazzafan zazzabin don tabbatar da basu dauke da cutar ta Ebola. REUTERS / Kenny Katombe
Talla

Gwamnan Arewacin Kivu, Julien Paluku ya ce an samu sabuwar cutar ce a yankin sa, kusa da iyakar Uganda, inda ya bukaci al’ummar Yankin da su kwantar da hankalin su.

Ya zuwa yanzu hukumomi ba suyi cikaken bayani kan mutane nawa ne suka kamu da cutar ba, sai dai ma’aikatar lafiya ta ce akalla mutane 25 sun kamu da zazzabi mai zafi kusa da garin Beni, kuma an dauki jinin su domin gudanar da bincike a Kinshasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.