Bakonmu a Yau
Farfesa Umar Pate kan bukatar Robert Mugabe na kayar da Jam'iyyarsa a babban zaben kasar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:34
Yau 'Yan kasar Zimbabwe ke gudanar da zaben shugaban kasa, irin sa na farko bayan kawo karshen mulkin shugaba Robert Mugabe, wanda ya kwashe shekaru kusan 30 a karagar mulki.Shugaba Emmerson Mnangagwa mai shekaru 75 daga Jam’iyyar ZANU PF ta tsohon shugaban kasa Mugabe na fafatawa ne da Nelson Chamisa mai shekaru 40 a Jam’iyyar MDC ta marigayi Morgan Tsvangirai.Tsohon shugaban kasa Robert Mugabe ya bukaci masu kada kuri’a da su kori Jam’iyyar ZANU PF daga karagar mulki a ganawar da yayi da manema labarai.Mun tattauna da Prof Umar Pate na Jami’ar Bayero kuma ga tsokacin da yayi kan zaben.