Isa ga babban shafi
Zimbabwe

Mnangagwa ya yi wa jar fata alkawarin ba su kariya

Shugaban Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da ke neman kuri’ar jama’a a zaben da za a yi ranar 30 ga wannan wata na yuli, ya yi wa har fatar kasar alkawarin cewa ba wanda zai sake masu gonaki matukar dai ya yi nasara a zaben.

Emmerson Mnangagwa, président du Zimbabwe.
Emmerson Mnangagwa, président du Zimbabwe. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Mnagagwa wanda ke gabatar da jawabi ga wakilan jar fatar kasar a birnin Harare safiyar yau asabar, ya ce bai kamata su nuna wata fargaba dangane da makomarsu a wannan kasa ba.

A lokacin mulkin Robert Mugabe, gwamnati ta kaddamar da wani gagarumin shiri inda aka kwace dimbin filayen noma daga hannun jar fata tsiraru domin danka su a hannu bakake masu rinjaye, to sai dai matakin ya haddasa koma-baya ga sha’anin noma a wannan kasa, lura da yadda aka mika filayen a hannu wadanda ba su da niyar gudanar da aikin gona.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.