Maitre Boubacar Madougou kan zaben da aka yi masa na shugaban Jam'iyyar CDS Rahma a Nijar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:48
A jmahuriyar Nijar, Jam’iyyar CDS Rahma ta zabi Maitre Boubacar Madougou a matsayin sabon shugabanta na kasa baki daya, bayan da kotu ta yanke hukuncin dauri a gidan yari da ke haramta wa shugaban jam’iyyar Abdou Labo cigaba da rike wannan matsayi.CDS Rahma dai jam’iyya ce da ta mulki kasar Nijar daga shekarar 1993 zuwa 1996, to sai dai sakamakon rikicin shugabanci da take fama da shi, jam’iyyar ta fuskanci koma-baya sosai a fagen siyasar kasar ta Jamhuriyar Nijar.Bayan kammala zaben da aka yi wa Maitre Madougou Boubacar a matsayin sabon shugaban jam’iyyar, har yanzu akwai wasu da ke adawa da hakan, kuma na tambayi Maitre Madougou domin jin yadda zai yadda zai tunkari wannan batu.