Safarrar yara kanana daga kasashen yammacin Afrika zuwa Gabon
Lamarin safarrar yara kanana daga kasashen yammacin Afrika zuwa wasu kasashen nahiyar da suka hada da Gabon ya soma haifar da fargaba ga manyan kungiyoyin da ke kare hakokin bil adam a Afrika.
Wallafawa ranar:
Hukumar Unicef ta samar da wani sashe a kasar ta Gabon da ke da hurumin bai wa wadanan yara mafaka, kafin daga bisali a dawo da su kasashen su na asali.
Hukumar ta bayyana cewa da dama daga cikin mutanen da ake tsallakawa da su zuwa Gabon na gudanar da kananan ayyuka da suka hada da gadi, tallace-tallace, yin jagora ga marasa gani da sauran su.
Akalla yara 80 ne hukumomin kasar suka tabbatar da ganowa da kuma ake kokarin dawo da su kasashensu na asali da suka hada da Najeriya, Benin, Togo da Nijar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu