Majalisar Dinkin Duniya ta aike da Manzo zuwa Algeria
Manzo na Majalisar Dinkin Duniya kan rikicin yammacin Sahara Horst Koehler ya gana da ministan Algeriya na harakokin waje Abdel Kader Messahel a wata ziyara da ya kadamar zuwa yankin da nufi sake dawo da kasashen Morocco da kungiyar Polisario a teburin tattaunawa.
Wallafawa ranar:
Jami’in na Majalisar Dinkin Duniya zai yi amfani da wannan dama domin ziyartar wasu sansanonin yan gudun hijira na yan Sarraoui a Tindouf dake kudu maso yammacin yankin wanda ke a matsayin cibiya ga kungiyar ta Polisario.
Morocco ta kama yankin yammacin Sahara ne a shekara ta 1975 bayan ficewar turayan mulkin malaka na kasar Spain, wanda tun a lokacin ne kungiyar Polisario ta shiga yakin neman samun yancin kai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu