Isa ga babban shafi
Kamaru

Kamaru ta tabbatar da mutuwar Jami'an tsaro 81 a rikicin 'yan aware

Daga lokacin da fada ya barke tsakanin ‘yan aware da kuma dakarun gwamnatin Kamaru, akalla jami’an tsaron kasar 81 ne suka rasa rayukansu kamar dai yadda alkalumma ke nunawa.

Gwamnatin kasar ta ce ana bukatar sama da cfa milyan dubu 12 kimanin Euro milyan 20 domin gudanar da ayyukan jinkai a yankin
Gwamnatin kasar ta ce ana bukatar sama da cfa milyan dubu 12 kimanin Euro milyan 20 domin gudanar da ayyukan jinkai a yankin STRINGER / AFP
Talla

Sojoji 74 da kuma ‘yan sanda 7 ne suka hallaka daga karshen shekarar bara zuwa yau a cewar wasu alkalumman ma’aikatar tsaro da kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ta samu kofinsa.

Har ila yau alkalumman na nuni da cewa akwai fararen hula sama da dari daya da suka rasa rayukansu a wannan rikici da ke faruwa a yankin arewa maso yamma da kuma kudu maso gabashin kasar ta Kamaru.

Wasu daga cikin abubuwa na assha da suka fara sakamakon wannan rikici sun hada da kone makarantun boko 120 wadanda gwamnatin ta ce ‘yan aware ne suka kona su.

Gwamnatin kasar ta ce ana bukatar sama da cfa milyan dubu 12 kimanin Euro milyan 20 domin gudanar da ayyukan jinkai a yankin

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.