Isa ga babban shafi
Libya

Wani hari ya halaka dakarun Haftar a Libya

Wasu tagwayen bama-bamai da aka tayar a garin Derna na kasar Libya, sun yi sanadiyyar mutuwar da kuma raunana wani adadi na dakarun Janar Khalifa Haftar da ke rike da muhimman yankunan gabashin kasar.

Janar Khalifa Haftar na kasar Libya
Janar Khalifa Haftar na kasar Libya Abdullah DOMA / AFP
Talla

Wani jami’i a yankin mai suna Khalifa al-Abidi, ya ce ga alama magoya bayan kungiyar IS ne suka kai harin a dai dai lokacin da mayakan na Haftar ke kokarin kakkabe su daga garin na Derna.

Janar Khalifa Haftar, hafsan sojin da ke rike da muhimman yankuna a kasar Libya, kafin cirawar sa zuwa Faransa domin neman magani ya umurci dakarunsa da su hana wa jiragen ruwan kasashen ketare matsowa kusa da gabar ruwan kasar.

Tun bayan kisa da kuma kawar da marigayi Muammar Ghadafi daga madafan ikon Libya, kasar ta fada cikin rikici.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.